Isra'ila ta yi barazanar kaiwa Hamas hare-hare a Zirin Gaza
Rundunar sojin Isra’ila ta yi gargadin zata iya kai farmaki akan wasu yankunan da ke cikin zirin Gaza, wadanda ta ce ‘yan ta’adda sun yi kakagida a wuraren.
Wallafawa ranar:
Daya daga cikin manyan jami’an sojin Isra’ila Birgediya Janar Manelis ya shaidawa manema labarai cewa kungiyar Hamas da yankin Zirin Gaza, ta fake ne da zanga-zangar Falasdinawa da ke gudana wajen kai hare-hare cikin Isra’ila.
Gargadin na Isra’ila ya zo jim kadan bayanda Falasdinawa suka yi jana’izar ‘yan uwansu 16 da sojin Isra’ila suka hallaka yayin arrangama da jami’an tsaron, a lokacin zanga-zangar da suka fara tun a ranar Juma’a akan iyakar Isra’ila da Zirin Gaza.
A halin yanzu yawan Falasdinawan da suka jikkata yayin zanga-zangar ya karu zuwa 70.
Dubban Falasdinawa ne ke zanga-zangar neman tilas Isra’ila ta kyale falasdinawa su koma yankunan da a yanzu ta mamaye.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu