Isa ga babban shafi
Cambodia

Daurin rai da rai zuwa wasu jami'an Khmer Rouge

Kotu a Cambodia ta yanke hukuncin daurin rai-da-rai a kan wasu manyan jami’an tsohuwar gwamnatin kasar ta Khmer Rouge su biyu saboda samun su da laifin azaftar da jama’a lokacin mulkinsu tsakanin 1975-1979.

Cambodia,shekaru 20 bayan  Pol Pot
Cambodia,shekaru 20 bayan Pol Pot RFI
Talla

Hukuncin da ta yanke a wannan juma’a, kotun ta samu wani mai suna Nuon Chea da lafin aikata kisan kiyashi a kan kabilar Chma musulmai tsiraru ‘yan kasar da kuma Khieu Samphan wanda ya aikata irin wannan laifi a ka ‘yan kabilar Vietnam lokacin mulkinsu.

Kungiyoyi kare dan Adam da dama ne suka gamsu da wannan hukunci da kotu ta yanke zuwa mutanen.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.