Isa ga babban shafi
Gabas ta Tsakiya

Isra'ila da Falasdinawa sun dakatar da kaiwa juna farmaki

Shugabannin Falasdinawa sun amince da shirin tsagaita wuta da Israila da safiyar yau Litinin, bayan jerin kazaman hare-haren da bangarorin biyu suka rika kaiwa juna, wadanda suka yi sanadiyar rasa rayuka.

Wani yankin birnin Gaza da jiragen yakin Isra'ila suka kaiwa farmaki, a matsayin martani kan hare-haren da mayakan Falasdinawa na Islamic Jihad suka kai mata da makaman roka.
Wani yankin birnin Gaza da jiragen yakin Isra'ila suka kaiwa farmaki, a matsayin martani kan hare-haren da mayakan Falasdinawa na Islamic Jihad suka kai mata da makaman roka. AFP / MAHMUD HAMS
Talla

Kasar Masar ce ta jagoranci tattaunawar tsagaita wutar da aka kulla da misalin karfe 4.30 na asubahin yau, kamar yadda jami’an kungiyar Hamas da na Islamic Jihad suka bayyana.

Zuwa yanzu hukumomin Israila basu ce komai ba kan yarjejeniyar, sai dai rahotanni sun ce an dakatar da kai hare hare daga kowanne bangare.

Wissam Zoghbar, wani jami’in kungiyar Falsdinu yace cikin yarjejeniyar tsagaita wutar harda sakin mara ga hanyoyin shiga Gaza da wuraren kamun kifin Falasdinawa da kuma inganta samar da wutar lantarkin Yankin.

Akalla Falasdinawa 23 aka kashe a fafatawar, yayin da aka kashe Yahudawa 4.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.