Amurka ta kulla kwarya-kwaryar yarjejeniyar zaman lafiya da Taliban
Kasar Amurka ta gabatar da kunshin kwarya-kwaryar yarjejeniyar zaman lafiyar da ta kulla da kungiyar Taliban a Afghanistan, yarjejeniyar da ake fatan ta takaita tashe tashen hankula da musayar wuta daga bangarorin biyu na tsawon mako guda a fadin kasar.
Wallafawa ranar:
Wani jami’in gwamnatin Amurka ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa cewar, takaita tashin hankalin nada matukar muhimmanci, kuma ya shafi bangarori da dama har da na gwamnatin Afghansitan.
Rundunar sojin Amurka wadda ke da jami’ai tsakanin 12,000 zuwa 13,000 a cikin Afghansitan za su sanya ido kan abubuwan da ke faruwa domin tabbatar da cewar mayakan Taliban na aiwatar da yarjejeniyar.
Jami’in ya ce Sakataren harkokin wajen Amurka Mike Pompeo ya tattauna kan cigaban da aka samu tare da shugaba Ashraf Ghani a taron tsaron da ke gudana a birnin Munich na kasar Jamus.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu