Isa ga babban shafi
Turkiya-Syria

Turkiya ta rasa dakarun ta 33 a Syria

Gwamnan jihar Hatay a Turkiya dake iyaka da Syria Rahmi Dogan ya ce akalla dakarun kasar Turkiyan 33 ne suka halaka yayin wani farmakin jiragen yaki, da ake kyautata zaton sojin Syria ne suka kai a lardin Idlib.

Wani sashi na garin Ras al-Ain dake lardin Hasakeh a arewacin Syria, inda dakarun Turkiya ke barin wuta kan mayakan Kurdawa.
Wani sashi na garin Ras al-Ain dake lardin Hasakeh a arewacin Syria, inda dakarun Turkiya ke barin wuta kan mayakan Kurdawa. SANA / AFP
Talla

Asarar rayukan gwamman sojin na Turkiya dai na zuwa makwanni bayan tsamin da dangantakarsu ta yi da Rasha kan farmakin da sojin Syrian ke kaiwa ‘yan tawaye a Lardin na Idlib dake zaman tungar karshe a garesu.

Tuni dai majalisar dinkin duniya ta yi gargadin cewar barazanar kazancewar sabon yaki a Syria na karuwa a duk bayan sa’a 1.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.