Isa ga babban shafi
Falasdinawa - Isra'ila

Falasdinu ta caccaki kasashen Larabawan da suka maido da hulda da Isra'ila

A Lahadin nan ministan harkokin wajen Falasdinu Riyad al-Maliki ya caccaki kasashen da suka maido da huldar diflomasiyya da Israila a shekarar da ta gabata, a daidai lokacin da tashin hankali ke dada kamari tsakanin Falasdinawa da Yahudawa.

 Ministan harkokin wajen Falasdinu, Riyad al-Maliki.
Ministan harkokin wajen Falasdinu, Riyad al-Maliki. Arif Yaman/Pool via Reuters
Talla

Al-Maliki ya shaida wa wani taron gaggawa na kungiyar kasashen Musulmai ta duniya cewa maido da huldar diflomasiyya da Isra’ila ba tare da samun kwanciyar hankalin da ake bukata ba na alamta goyon baya ga cin zalin da Yahudawa ke yi.

Kasashen da suka maido da huldar diflomasiyya da Isra’ila dai su ne: Sudan, Morocco, Hadaddiyar Daular Larabawa da Bahrain.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.