Isa ga babban shafi
Afghanistan - Turkiya

Turkiya za ta kai dakarunta Afghanistan bayan janyewar Amurka - Erdogan

Shugaban Turkiya Racep Tayyip Erdogan ya ce kasar sa ce kadai za ta iya tabbatar da tsaro a Afghanistan idan Amurka ta kammala janye dakarunta daga kasar.

Shugaban Turkiya Racep Tayyip Erdogan.
Shugaban Turkiya Racep Tayyip Erdogan. via REUTERS - MURAT CETÄ°NMUHURDAR/PPO
Talla

Erdogan ya bayyana haka ne a yayin da yake shirin ganawa da shugaban Amurka Joe Biden, batun da ya ce za su tattauna akai.

Shugaban na Turkiya ya bada tabbacin cewar a shirye yake ya girke dakarunsa da bada tsaro a filin jiragen sama na Kabul babban birnin Afghanistan, inda ke zama babbar hanyar shige da ficen jami’an Diflomasiyya da ma’aikatan agaji a kasar.

Ranar Asabar kungiyar Taliban ta gargadi kasashen ketare da kada su kuskura su sake girke dakarunsu a Afghanistan bayan janyewar dakarun Amurka da na kungiyar NATO, inda kungiyar ta ce nauyin baiwa ofisoshin jakadancin kasashen ketare da filayen jiragen sama zai koma kan ‘yan kasar ta Afghanistan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.