'Yan sandan Isra'ila sun harbe wani Bafalasdine da ya kai musu hari
Rundunar ‘yan sanda Isra’ila ta ce jami’anta sun kashe wani Bafalasdine bayan da ya daba wa wani jami’i wuka a yau Lahadi.
Wallafawa ranar:
Mutumin ya tinkari jami’an ‘yan sandan da ke gadi a kofar Bab Huta a Birnin Kudus, inda ya zaro wuka ya daba wa daya daga cikinsu, a cewar sanarwar da rundunar ta fitar, tana mai cewa an harbe maharin mai shekaru 19 har lahira.
Sanarwar maharin ya ji wani dan sanda rauni, kuma an dauki gaba dayansu zuwa asibiti don yi musu magani.
Kofar Bab Huta dai hanya ce da ka iya kai mai bin ta Masallacin Al-Aqsa, wajen na 3 mai tsarki ga mabiya addinin Islama, inda mummunar tarzoma ta tashi a watan Mayun 2021 bayan da ’yan sandan isra’ila suka shiga harabarta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu