Isa ga babban shafi
Koriya ta Arewa-Korona

Korona ta kashe mutane 21 a Koriya ta Arewa a cikin sa'o'i 24

Koriya ta Arewa ta sanar da nutuwar mutane 21 a Asabar din nan, kana ta ce mutane rabin miliyan ne suka kwanta rashin lafiya  a fadin kasar, kwanaki 2 bayan da ta tabbatar da sake bullar cutar Covid 19.

Shugaban Koriya ta Arewa ,Kim Jong-un.
Shugaban Koriya ta Arewa ,Kim Jong-un. JUNG Yeon-Je / AFP
Talla

Duk da kakaba dokokin kulle don dakile yaduwar cutar  a tsakanin al’ummarta wadda da ba a wa rigakafi ba, Koriya  ta Arewa tana samun dubban masu harbuwa da wannan cutar a duk rana.

A ranar Juma’a kadai, sama da mutane miliyan 174,440 ne suka kamu da cutar, kuma dubu 81, 430 sun murmure, a yayin da 21 suka mutu, kamar yadda kamfanin dillancin labarn Koriya ta Arewar ta ruwaito.

A ranar Alhamis Koriya ta Arewar ta tabbatarda cewa an samu bullar Omicron, nau’in cutar Covid-19 mai saurin yaduwa a babban birnin kasar Pyonyang, inda shugaba Kim Jong Un ya yi umurnin dokar kulle  a kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.