Isa ga babban shafi

Kasashen da ke cikin yarjejeninyar Abraham Accord za su yi taro a Bahrain

Jami'an diflomasiya daga Amurka da Israila da wasu kasashen Larabawa 4 za su taru yau a Bahrain domin tattauna ci gaban da aka samu a karkashin shirin zaman lafiyar Gabas ta Tsakiya da aka yiwa lakabi da ‘Abraham Accord’.

Shugaban Amurka Joe Biden.
Shugaban Amurka Joe Biden. POOL/AFP/File
Talla

Ana saran taron ya samu halartar jami’an ma’aikatar harkokin wajen kasashen Daular Larabawa da Bahrain da Morocco wadanda suka kulla yarjejeniyar hulda da Israila a shekarar 2020, sai kuma Masar wadda tun a shekarar 1979 take hulda da kasar.

Ita dai wannan yarjejeniyar da ake kira ’Abraham Accord’ ta harzuka Falasdinawa wadanda suka zargi kasashen Larabawan da suka sanya hannu a ciki da cin amana.

Kasar Amurka ta ce ta na bukatar gudanar da irin wannan taro kowacce shekara da zummar sasanta Yahudawa da Falasdinawa domin tabbatar da zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.