Isa ga babban shafi

Harin kunar bakin wake ya kashe mutane 25 yayin wani taron addini a Pakistan

Rahotanni daga Pakistan na cewa akalla mutane 25 sun mutu a harin kunar bakin wake da aka kai yayin wani taron addini yau Juma’a a lardin Balochistan na kasar.

Makamantan hare-haren ba sabon abu ba ne a Pakistan.
Makamantan hare-haren ba sabon abu ba ne a Pakistan. © (c) 2023 Thomson Reuters
Talla

Karamin ministan lardin na Balochistan Zubair Jamali ya tabbatar da cewa mutane 25 sun mutu nan ta ke sai kuma wasu fiye da 80 da suka jikkata.

A cewar minista Jamali cikin jerin wadanda suka jikkata har da wasu 20 da ke cikin mawuyacin hali, lamarin da ya sanya fargabar yiwuwar karuwar mamata a harin na yau.

Rahotanni sun bayyana cewa dan kunar bakin waken ya yi damarar bom tare da shiga cikin dandazon mutanen da ke halartar taron addinin na Yau juma’a.

Ko a watan Yulin da ya gabata, sai da wani harin ta’addanci ya hallaka sojojin Pakistan 12 a Lardin na Bolichistan kari kan kisan jami’an tsaro 9 cikin watan Maris duk dai a yankin mai fama da matsalar tsaro.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.