Isa ga babban shafi
Iraqi

Kusan Mutane 70 sun mutu a hare haren kasar Iraqi

Wasu Jerin bama bamai sun tashi yau Alhamis cikin Bagadaza babban birnin kasar Iraqi, inda suka hallaka kusan mutane 70, abinda ya kawo adadin mutane da aka kashe zuwa kusan 300 a cikin makwanni biyu.

Reuters
Talla

An dai kai hare haren na yau ne a Sadr.

Rahotanni sun ce, harin na farko an kai shi ne a inda leburori ke jiran motar hawa, inda wani mai babur ya zo ya tada bam.

Hare haren kuma na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun rashin fahimtar juna tsakanin 'yan Shi'a da Sunnah, abinda ke barazana ga Gwamnatin hadin kan kasar.

Daga ranar 15 ga watan da ya gabata na Disamba, da aka samu hare haren da suka kashe mutane sama da 60 a cikin kasar, zuwa wanan rana, an samu munanan hare hare guda takwas, wadanda suka hallaka kusan mutane 300.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.