Isa ga babban shafi
Iran-IAEA-UE-USA

Za'a sake yin wani sabon zagayen tattauna shirin nukliyar kasar Iran

Kasar Iran da manyan kasashen duniya 6, sun amince su sake yin wani zagayen tattaunawa dangane da aikin nukiliyar Iran, wanda kasashen duniya ke zargin cewa na makamai ne, ba na samar da makamashi ba.

wakilin kasar Iran da na gungun kasashe 6 masu tattaunawa kan shirin Iran na Nukliya a ranar  23 mai 2012.
wakilin kasar Iran da na gungun kasashe 6 masu tattaunawa kan shirin Iran na Nukliya a ranar 23 mai 2012. REUTERS/Government Spokesman Office/Handout
Talla

Jakadiyar harakokin wajen Kungiyar tarayyar Turai Uwargida Cathrine Aston ce, ta bayyana haka, sai dai bata yi wani karin haske ba, dangane da yadda bangarorin 2 suka cimma wannan yarjejjeniya.

Sai dai kuma wasu majiyoyin sun bayyana cewa, manyan kasashen dunioyar guda 6 dake da ruwa da tsakki kan aikin nukiliyar kasar ta Iran wadanda suka hada da kasar Britania, China, Faransa, Russia, Amirka da kuma kasar Jamus za su ci gaba da zama tare da kasar ta Iran domin kara samun haske kan zargin da ake yi mata.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.