Isa ga babban shafi
Syria-MDD

Wakilan MDD za su isa kasar Siriya

Majalisar Dinkin Duniya tace, nan da ‘yan kwanaki ne wakilanta zasu shiga cikin kasar Syria domin tabbatar da zargin anfani da makamai masu guba, da aka haramta amfani da su a karkashin dokokin duniya. Majalisar ta Dinkin Duniya ta kuma ce Shuaban Syria Bashar al-Assad, ya amince ya ba wakilan damar shiga yankuna kasar guda uku da aka ruwaito an yi amfani da makamai masu guba a rikicin kasar da aka kwashe fiye da watanni 28 ana gwabzawa.Idan dai har aka gano ana amfani da makaman masu guba, Majalisar na iya bude kofar taimakawa ‘Yan tawaye, da makaman da za su yaki dakarun gwamnatin kasar. 

Shugaban kasar Syria, Bashar al- Assad
Shugaban kasar Syria, Bashar al- Assad 路透社
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.