Hukumar dake haramta yaduwar makamai masu guba za ta tura tawaga ta biyu zuwa Syria
Hukumar dake haramta yaduwar makamai masu guba a duniya ta ce za ta tura tawaga ta biyu ta kwararrun zuwa Syria domin cimma burinta na lalata makaman Syria.
Wallafawa ranar:
Hukumar ta bayyana hakan ne a wata rubutacciyar sanarwa da ta fitar a yau Litinin ta na mai cewa hakan zai karawa tawagar farko karfi wajen gudanar da aikin.
“Haka zai taimaka wajen ganin mun tabbatar da cewa an lalata makaman.” Kamar yadda sanarwar ta fitar.
Tun makon da ya gabata ne tawagar farko ta isa
kasar inda ta fara gudanar da ayyukanta.
An dai ba hukumar wa’adin daga nan zuwa tsakiyar shekarar 2014 domin ta lalata makaman na Syria a karkashin wata amincewa da Majalisar Dinkin Duniya ta yi a watan da ya gabata.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu