Majalisar Dinkin Duniya
Hukumar Abinci Ta Duniya na fuskantar gibin kudin tafiyar da ayyukanta
Hukumar Samar da abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce za ta katse tallafin abincin da take bai wa wasu kasashen duniya, saboda gibin dala bilyan guda da hukumar ta samu a cikin kasafin kudadenta.
Wallafawa ranar:
Talla
Daraktan hukumar, Ertharin Cousin, ta ce sakamakon raguwar kudaden ya sa sun zabtare taimakon da ya kamata su bai wa kasashen Haiti, Niger, Mali da Kenya.
Jami’ar hukumar ta ce ayyukansu na dada fadada, sakamakon karuwar mabukata musamman a Syria inda take neman ciyar da mutane sama da miliyan hudu akan kudi dala miliyan 40, yayin da kudaden ta na raguwa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu