Isa ga babban shafi
Najeriya-Pakistan

Malala: Mayakan Boko Haram sun jahilci Musulunci

Dalibar Makarantar Pakistan Malala Yousafzai, da ‘Yan Taliban suka harba tace ‘Yan mata sama da 200 da Mayakan Boko Haram suka sace a Najeriya tana ganinsu tamkar ‘Yan uwanta ne a tattaunawarta da Kafar CNN.

Malala Yousafzai da ke gwagwarmayar tabbatar da ilimin 'yaya mata a Pakistan
Malala Yousafzai da ke gwagwarmayar tabbatar da ilimin 'yaya mata a Pakistan REUTERS/Gary Cameron
Talla

Malala da ke gwagwarmayar tabbatar da ilimin Mata, tace Mayakan Boko Haram sun jahilci addinin Islama kuma wadanda ba su san ilimin Al Qaur’ani ba.

Malala tace a lokacin da ta ji labarin an sace Mata a Najeriya sai ta ji kamar ‘Yan uwanta ne ke rayuwa a gidan yari.

A shekarar 2012 ne Mayakan Taliban suka harbi Malala saboda gwagwarmayarta na tabbatar da ilimin ‘ya’ya mata a kasar Pakistan, inda yanzu haka kuma ta ke rayuwa a Birtaniya bayan ta samu sauki.

Akwai manyan kasashen duniya yanzu da suka yi alkwalin za su taimakawa Najeriya domin kubutar da Matan sama da 200 da aka sace a Chibok cikin Jahar Borno da ke arewa maso gabacin Najeriya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.