Isa ga babban shafi
Masar-Falasdinawa

Gaza: Masar tana karbar ‘Yan gudun hijira

Gwamnatin kasar Masar ta bude kan iyakar Rafah da ake shiga Gaza domin karbar Falasdinawan da suka jikkata a hare haren da Isra’ila ke kai wa a Zirin Gaza. Kamfanin Dillacin labaran Masar ya ruwaito cewa nan gaba likitoci zasu fara karbar Falasdinawa a wata asibiti da ke arewacin Sinai, kan iyaka tsakanin Gaza da Isra’ila.

Falasdinawa a kan iyakar Rafah, tsakanin Masar da Gaza
Falasdinawa a kan iyakar Rafah, tsakanin Masar da Gaza REUTERS/Ibraheem Abu Mustafa
Talla

Amma Rafah nan ne mashigin da ake isa Gaza ba tare ketawa Isra’ila ba.

Kimanin mutane 70 aka ruwaito sun mutu tun lokacin da Isra’ila ta fara luguden wuta da jiragen sama a  Zirin Gaza.

Likitoci sun ce yawancin wadanda suka mutu mata ne da yara kanana.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.