Isa ga babban shafi
Isra'ila-Falesdinawa

Isra’ila da Hamas sun tsagaita wuta na sa’o’I 12

Sakataren harakokin wajen Amurka John Kerry da manyan Jami’an diflomasiyar Turai da na gabas ta tsakiya sun yi kira ga Isra’ila da Hamas su tsawaita wa’adin yarjejeniyar tsagaita wuta ta sa’o’I goma sha biyu da suka amince kuma wadda ta fara aiki a yau Assabar.

Ministan Harakokin wajen Faransa Laurent Fabius yana jawabi tare da wakilan kasashen Amurka da turkiya da Birtaniya da Jamus da Italiya bayan sun gana game da rikicin Gabas ta tsakiya a birnin Paris.
Ministan Harakokin wajen Faransa Laurent Fabius yana jawabi tare da wakilan kasashen Amurka da turkiya da Birtaniya da Jamus da Italiya bayan sun gana game da rikicin Gabas ta tsakiya a birnin Paris. REUTERS/Gonzalo Fuentes
Talla

Isra’ila da Hamas dukkaninsu sun amince su tsagaita wuta ta tsawon sa’o’I goma sha biyu ga hare haren da suke kai wa juna a rikicin Gaza domin samun shigar da kayan jin kai ga Falasdinawa.

An shafe kwanaki 19 Isra’ila na kai wa Falasdinawa hari, kuma zuwa yanzu Kusan Falasdinawa 1,000 suka mutu a hare haren da Isra’ila a Gaza.

Jimillar Sojojin Isra’ila 37 ne suka mutu a rikici tsakaninsu da Mayakan Hamas na Falasdinawa.

Ministan harakokin wajen Faransa Laurent Fabius ya yi kira ga bangarorin biyu su tsawaita yarjejeniyar tsagaita wuta ta sa’o’I 12 da suka amince  kamar yadda ya shadaiwa manema labarai bayan sun kammala tattaunawa da wakilan manyan kasashen duniya  game da rikicin Gaza.

Isra’ila da Hamas dai sun amince su tsagaita wuta na wucci gadi saboda dalilai na jin kai, suna masu watsi da duk wani mataki na amincewa su tsagaita wuta mai dorewa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.