Faransa-Afrika ta Tsakiya
An sace wata Bafaransa a Afrika ta tsakiya
Fadar Shugaban Kasar Faransa ta sanar da cewa wasu ‘Yan bindiga sun sace wata ‘Yar kasar mai shekaru 67 da ke aikin agaji a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya. Faransa ta yi allawadai da matakin inda ta bukaci wadanda suka sace Baturiyar su gaggauta sakinta cikin gaggawa. Bayani sun ce yanzu haka ofishin Jakadancin Faransa da ke Bangui na tattaunawa da shugaban kiristocin birnin domin tuntubar a wadanda suka sace matar.
Wallafawa ranar:
Talla
Ana dai zargin Mayakan anti balaka ne suka sace jami'ar agajin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu