Isa ga babban shafi
Syria

An kashe ministan labaran IS a Syria

Ma’aikatar tsaron Amurka ta bayyana cewa, wani harin jiragen sama da aka kai a Syria, ya kashe ministan yada labaran kungiyar IS mai da’awar jihadi.  

An kashe daya daga cikin jagororin kungiyar IS ya mutu a harin sama da aka kaddamar a Syria
An kashe daya daga cikin jagororin kungiyar IS ya mutu a harin sama da aka kaddamar a Syria
Talla

Mai magana da yawun ma’aikatar Peter Cook ya ce, a ranar 7 ga watan Satumba ne, rundunar hadin gwiwar ta kashe Wa’il Adil Hassan Salman al-Fayad, wanda aka fi sani da Dr. Wa’il a kusa da birnin Raqa.

Dr. Wa’il dai, shi ne mai kula da fayafayen bidiyon farfaganda da kungiyar ke yadawa, in da ta ke nuna yadda take azabtar da mutane da kuma fille kawunansu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.