Isa ga babban shafi
MDD

An kaddamar da gidauniyar taimaka wa Sahel

Majalisar Dinkin Duniya ta kaddamar da gidauniyar Dala biliyan kusan 3 don taimaka wa mutanen kasashen da ke yankin Sahel da rikicin Boko Haram ya shafa, abin da ya jefa su cikin mawuyacin hali. 

Mutanen da rikicin Boko Haram ya shafa na bukatar agaji
Mutanen da rikicin Boko Haram ya shafa na bukatar agaji AFP PHOTO/FAROUK BATICHE
Talla

Wannan na zuwa ne a dai dai lokacin da Majalisar ke cewa, talauci da yunwa da gurbacewar yanayi zai shafi mutane akalla miliyan 15 a wannan yankin.

Ofishin da ke kula da ayyukan agajin gaggawa na Majalisar ya ce, kashi 40 cikin 100 na kudaden za a yi amfani da su ne wajen tallafa wa mutane miliyan 7 da rikicin Boko Haram ya shafa a arewa maso gabashin Najeriya.

Wata kididdiga ta nuna cewa, akalla mutun guda daga cikin mutane shida a yankin Sahel na fama da yunwa, yayin da kuma kananan yara da dama ba sa samun wadataccen abinci mai gina jiki a yankin.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce, karuwar mutanen da ke tsere wa gidajensu saboda tashin hankali a yankin Sahel, ta tsananta matsalar kwararar 'yan gudun hijira a Turai da kuma shiga kungiyoyin ‘yan ta’adda.
 

Masu bukatar  agaji a Afrika za su karu, matukar adadin yawan al'ummar nahiyar ya kai sama da biliyan 2 nan da shekarar 2050, kamar yadda Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.