Iran
Ambaliyar Ruwan Sama Ta kashe Mutane 35 a kasar Iran
A kasar Iran, mutane 35 suka gamu da ajalinsu sakamakon ambaliyar ruwan sama, yayinda wasu mutanen takwas har yanzu ba’a san inda suka makale ba.
Wallafawa ranar:
Talla
Kafofin yada labarai dake kasar musamman gidajen Talabijin sunyi ta nuna hotunan barnar da ambaliyar ruwan ta yi.
Bayanai na cewa an sami ambaliyan ruwan saman a dukkan yankuna na kasar.
Rahotanni na nuna tun jiya Juma'a ake shatata ruwan sama a wasu sassan kasar da fasa kananan kwalbatoci da mamaye hanyoyi da gidaje da tafiya da motoci da aka ajiye a gefen hanya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu