Isa ga babban shafi
Venezuela

Gobara ta hallaka Fursunoni 68 a Venezuela

Hukumomin Kasar Venezuela sun ce gobara a wani wurin da yan sanda ke tsare wadanda ake zargi da aikata laifufuka ta yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 68, yayin da wasu da dama suka jikata lokacin da wasu da ake tsare da su suka yi yunkurin tserewa.

Wasu daga cikin iyalan da suka rasa mutane su a tashar yan Sanda
Wasu daga cikin iyalan da suka rasa mutane su a tashar yan Sanda REUTERS/Carlos Garcia Rawlins
Talla

Babban mai gabatar da kara, Tarek Williams Saab ya ce sakamakon wannan hadari da aka samu a tashar yan sandar dake Carabobo sun nada masu bincike guda 4 domin binciko abinda ya faru.

Carlos Nieto, shugaban wata kungiyar agaji, ya ce wasu daga cikin mutanen dake wurin sun kone kurmus, yayin da wasu kuma hayaki ne ya kashe su.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.