Isa ga babban shafi
Turkiya-AMurka

Amurka ta janye takunkumin da ta kakaba wa Turkiya

Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da dage takunkumin karayar tattalin arziki da ya kakaba wa Turkiya, inda kuma ya kare kansa daga daukar matakin janye dakarunsa daga Syria.

shugaban Turkiya, Recep Erdogan tare da shugaban Amurka, Donald Trump
shugaban Turkiya, Recep Erdogan tare da shugaban Amurka, Donald Trump Murat CETINMUHURDAR / TURKISH PRESIDENTIAL PRESS SERVICE / AFP
Talla

Shugaban ya bukaci Hukumar Baitul-malin Amurka da ta cire dukkan takunkumin da aka  malkaya wa Turkiya a ranar 14 ga wannan wata na Oktoba saboda hare-haren da gwamnatin RecepTayyip Erdogan ke kaddamarwa kan mayakan Kurdawa a yankin arewa maso gabashin Syria.

A cewar Trump "wannan takunkumin zamu cire shi, sai idan har an sake samun wata matsalar da ba mu ji dadi ba".

"Na yi magana da jagoran Kurdawa, kuma ya nuna matukar godiya saboda matakin Turkiya na dakatar da hare-harenta". In ji Trump.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.