Isa ga babban shafi
Amurka

Ina aka kwana kan batun tsige Trump a majalisar dattawar Amurka?

Shugabar Majalisar dokokin Amurka Nancy Pelosi taki bayyana lokacin da zata mikawa Majalisar Dattawa takardun bukatar tsige tsohon shugaban kasa Donald Trump domin ganin ya fuskanci hukunci, duk da adawar da Jam’iyyar Republican keyi kan bukatar, yayın da sabon shugaban kasa Joe Biden ya bukaci hadin kan jama’a.

Tsohon shugaban Amurka Donald Trump
Tsohon shugaban Amurka Donald Trump REUTERS/Carlos Barria
Talla

Pelosi tace tsohon shugaban ya aikata babban laifi wajen tinzira jama’a suyi bore da kai hari Majalisar, inda har mutane 5 suka mutu, saboda haka babu dalilin da za’a kauda ido ba tare da daukan mataki akan sa ba.

Shugaban 'Yan Jam’iyyar Republican a Majalisar Mitch McConnell ya bar kofa bude wajen ganin an hukunta tsohon shugaban, amma Sanata Lindsey Graham na hannun daman tsohon shugaban yace allura na iya tono garma wajen binciken tsohon shugaban.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.