FIFA na goyan bayan fadada gasar cin kofin kungiyoyi - Infantino
Shugaban Hukumar Kwallon kafa ta Duniya FIFA Gianni Infantino ya bayyana mutukar goyan bayan sa ga fadada gasar cin kofin kungiyoyi na duniya.
Wallafawa ranar:
Infantino wanda ya bayyana goyan bayan nasa yayin zantawa a wata hira da kamfanin dillacin labaran Faransa na AFP da zunnan yace, hakan wata hanyace ta bunkasa gasar kasa da kasa tsakanin kungiyoyi.
Yana mai cewa maimakon kungiyoyi bakwai da suke wakiltan nahiyoyi, lokaci yayi da ya kamata a kara adadin.
Yanzu haka anasaran kungiyoyi 24 zasu fafata a gasar ta bana da kasar China zata karbi bakwanci ciki harsa kungiyoyi 8 daga nahiyar Turai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu