Mutane 49 ne suka mutu a wani hatsarin jirgin kasa a gabashin Taiwan
‘Yan sanda a Taiwan sun ce akalla mutane 49 ake fargabar sun rasa rayukansu sakamakon hatsarin jirgin kasan da ya auku a gabashin yankin da safiyar yau Juma’a.
Wallafawa ranar:
Talla
Akwai dai karin fargabar karuwar adadin mamatan, la’akari da cewar jami’ai na kan kokarin ceto wasu fasinjoji 72 da suke makale a taragan jirgin da yayi hatsarin, baya ga wasu 61 da suka jikkata.
Hukumomin yankin sun bukaci a gudanar da bincike cikin gaggawa don gano musababin aukuwar hatsarin da ya janyo asarar rayuka 49 a yankin na Taiwan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu