Dakarun Hamas sun tabbatar da hallaka wasu sojojin Isra'ila
Hukumomin Gaza sun tabbatar da hallaka wasu sojojin Israe’la bayan da suka harba rokoki, dai-dai kan iyakar yankin da Isra’ilan, a wani abu mai kama da ramuwar gayya.Tun makon da ya gabata dai rikici ke kara tsananta kusan kowacce rana, inda kasashen biyu ke harba makaman rokoki a tsakanin su, abinda ya yi sanadiyyar mutuwar Falasdinawa 56 da kuma yahudawa 6.
Wallafawa ranar:
Ya zuwa yanzu dai yahuwada 100 sun jikkata, a yayin da Falasdinawa kusan 250 ke kwance a gadon asibiti, sakamakon yadda ake musayar harba makamai a tsakanin juna.
Hamas
Itama kungiyar Hamas ta ce manyan kwamandojin ta da dama sun rasa rayukan su sakamakon hari ta sama da sojojin Isra’ila suke kaiwa yankin, cikin su kuwa har da babban kwamandan ta Bassem Issa.
Da yake jawabi bayan kisan Frime ministan Isra’ila Benjamin Natenyahu, ya ayyana kisan babban kwamandan a matsayin nasara, yana mai gargadi kan cewa rayukan Falasdinawa na cikin hadari.
Zamu ci gaba da yiwa Isra'ila luguden wuta
Sai dai kuma da take mayar da martani, kungiyar Hamas ta ce dakarunta sun shirya tsaf don yiwa sojojin Isra’ila luguden wuta.
Baya ga kisan sojojin Isra’ilan da suka mutu, Hamas ta kuma ce ta jikkata wani sojan Isra’ila daya.
Sojojin Gaza sun harba makaman roka zuwa Isra’ila sama da dubu 1 tun daga ranar litinin din makon jiya zuwa yanzu kamar yadda rundunar sojan Isra’ilan ta bayyana, sai dai itama ta ce ta hallaka manyan kwamandojin Hamas din da dama.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu