Isa ga babban shafi
Isra'ila-Falasdinu

Farmakin Isra'ila a kan Gaza ya halaka mutane sama da 40

Hare-haren da Isra’ila ke kai wa a yankin Zirin Gaza ya yi sanadin mutuwar Falasdinawa 40 a yau Lahadi,  wanda shine adadi mafi muni na wadanda suka mutu a rana guda a kai- ruwa -rana da aka shafe kusan mako guda ana yi, a yayin da kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ke  gudanar da taro a kan rikicin da ke ci gaba da ta’azzara.

'Yan jarida na daukar bayanai daga baraguzan ginin da ke kunshe da ofisoshin kafafen yada labarai da isra'ila ta rusa.
'Yan jarida na daukar bayanai daga baraguzan ginin da ke kunshe da ofisoshin kafafen yada labarai da isra'ila ta rusa. MOHAMMED ABED AFP
Talla

Yakin wanda shine  mafi muni tun bayan shekarar 2014, wanda ya tashi sakamakon rikicin da ya auku a birnin Kudus, ya haddasa musayar wuta daga bangarorin da ba sa ga- maciji da juna, inda yanzu wadanda suka mutu suka kai 181 a yankin Gaza tun daga ranar Litinin,  yayin da 10 suka halaka a bangaren Yahudawa, kamar yadda hukumomi suka sanar.

A Gaza, tawagogin ma’aikatan aikin agaji su na aiki tukuru wajen ciro gawarwakin mutane a baraguzan gine –gine da suka ruguje, a yayin da dangi da abokai ke kuka cikin makoki.

Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres  ya bayyana takaici da yadda lamarin ke shafar akasari fararen hula, da kuma yadda Isra’ila ke kai hare -hare ba kakkautawa

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.