Isa ga babban shafi
Gaza-Isra'ila

Kungiyar Hamas da Islamic Jihad sun amince da shirin tsagaita wuta da Isra'ila

Israila da kungiyar Hamas ta Falasdinawa da kuma Islamic Jihad sun bayyana amincewa da shirin tsagaita wutar da zai fara aiki daga karfe 2 na dare agogon yankin domin kawo karshen yakin da aka kwashe kwanaki 11 ana gwabzawa.

Wasu Sojin Hamas da ke mayar da martani kan hare-haren Isra'ila kan al'ummar yankin Gaza.
Wasu Sojin Hamas da ke mayar da martani kan hare-haren Isra'ila kan al'ummar yankin Gaza. AP - Adel Hana
Talla

Sanarwar da ofishin Firaministan Israila Benjamin Netanyahu ya gabatar ta ce majalisar tsaron Israila ta amince ba tare da hamayya ba shirin kasar Masar na tsagaita wutar ba tare da gindaya sharidodi ba.

Suma kungiyoyin Hamas da Islamic Jihad sun tabbatar da shirin zagaita wutar da zai fara aiki daga karfe 2 na daren yau agogon Gabas ta Tsakiya.

Zuwa yanzu dai Falasdinawa 332 suka rasa rayukansu galibinsu fararen hula ciki har da mata da kananan yara, a luguden makaman roka fiye da 100 da Sojin Isra'ila suka harbawa yankin Gaza cikin kwanaki 11 da aka yi ana rikicin.

Yadda hare-haren Isra'ila ya rutsa da tarin kananan yara a Gaza.
Yadda hare-haren Isra'ila ya rutsa da tarin kananan yara a Gaza. AP - Khalil Hamra

 

Haka zalika mutane fiye da dubu 1 da 600 suka jikkata yayinda ake fuskantar karancin abinci da magunguna a bangare guda kuma iyalai fiye da dubu 10 suka rasa matsugunansu sakamakon rushe-rushen da hare-haren na Isra'ila ya yiwa yankin.

 

Wani da harin Isra'ila ya rutsa da shi.
Wani da harin Isra'ila ya rutsa da shi. © AFP/Mohammed Abed MOHAMMED ABED

 

Matakin tsagaita wutar ya biyo bayan kiraye-kirayen kasashen Duniya don daukar matakin Diflomasiyya da nufin shawo kan rikicin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.