Saudiya
Wani dauke da makami ya yi yunkurin afkawa lilamin masallacin Harami
Wani Mutumin dake dauke da makami ya nemi kai hari kan limamin Masallachin Ka’abah dake kasar Saudiya yau Juma’a lokacin da yake hudubar sallar Juma’a.
Wallafawa ranar:
Talla
Hukumomin kasar sun ce mutumin dake dauke da makami ya nufin kan limamin ne yayin Sallar amma jami’an tsaro suka yi nasarar dakile harin.
Yanzu haka dai mutumin na can tsare a hannun jami’an tsaro inda yake bayani kan dalilin da ya sa shi wannan yunkuri.
Hukumomin Saudiya na tsaurara matakan tsaro a ciki da wajen masallatai masamman na Harami da Madina, saboda fargabar kaimu hari.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu