Isa ga babban shafi
Afghanistan

ISIS na shirin kai hari a filin jiragen sama na Kabul

Kasashen Amurka da Birtaniya da Australia na gargadin jama’arsu da ke Afghanistan game da yin balaguro zuwa filin jiragen sama na  birnin Kabul bayan wasu bayanan sirri sun nuna cewa, ‘yan ta’adda na shirin kaddamar da farmaki kan mai uwa da wabi.

Sojojin kasashen ketare masu samar da tsaro a filin jiragen sama na birnin Kabul a daidai lokacin da ake kwashe jama'a daga Afghanistan
Sojojin kasashen ketare masu samar da tsaro a filin jiragen sama na birnin Kabul a daidai lokacin da ake kwashe jama'a daga Afghanistan Wakil KOHSAR AFP/Archivos
Talla

Tuni Amurka da Australia da Birtaniya suka shaida wa ‘yan kasashensu cewa, su gaggauta ficewa  daga harabar filin jiragen saman na birnin Kabul.

Tun da farko shugaban Amurka Joe Biden ne ya yi gargadin cewa, akwai barazanar wasu tsageru masu alaka da mayakan ISIS za su kai harin.

Shi ma Ministan Kula da Ayyukan Sojojin Birtaniya, James Heappey ya  ce, a halin yanzu, akwai bayanan sirri masu inganci game da yiwuwar kaddamar da farmakin nan kusa, yana mai bukatar jama’ar da ke son ficewa da su dakatar da halartar filin jiragen sama na Kabul a yanzu.

Kodayake Heappey ya ce, za su yi iya bakin kokarinsu domin tabbatar da tsaron lafiyar jama’ar da ke dako a filin jiragen saman, amma za su sauya shawara da zaran sun samu sabbin rahotanni a cewarsa.

Tun da farko dai, mayakan Taliban sun yi alkawarin samar da tsaro a harabar filin jiragen saman, amma dai kasashen yammacin duniya ba za su yi sakaci da rahoton yiwawur kaddamar da farmakin ba daga ISIS kamar yadda wani jakada na kungiyar NATO ya shaida wa Reuters.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da aka kwashe akalla mutane dubu 80 daga Afghanistan don guje wa zalincin Taliban, kuma har yanzu akwai sauran dubbai da ke jiran ficewa daga kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.