Isa ga babban shafi
Rasha - Ukraine-MDD

Majalisar Dinkin Duniya za ta yi taruka kan rikicin Rasha da Ukraine

Majalisar dinkin duniya za ta gudanar da jerin taruka a wannan mako a kan rikicin Rasha da Ukraine,  sai dai babu wani karin haske a kan ko za a kai ga amincewa da wani daftari a hukumance.

Antonio Guterres, Sakataren Majalisar Dinkin Duniya.
Antonio Guterres, Sakataren Majalisar Dinkin Duniya. RFI
Talla

Majiyoyin diflomasiya sun  shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa cewa a ranar Litinin, kwamitin tsaro na majalisar  za ta tattauna batun tsarin tsaro a Turai, inda ake sa ran ministan harkokin wajen Poland, Zbigniew Rau ya gabatar da jawabi a yayin taron.

Duk da cewa taro ne na shekara shekara, zai mayar da hankali ne a kan yakin da ake a Ukraine, kuma mai yiwuwa ya sabanta kiraye kirayen lalubo zaman lafiya.

Kamfanin dillancin labaran Faransa ya ruwaito cewa ya jiyo wasu majiyoyi na dabam na cewa kwamitin zai duba batun matsalar  jnkai a Ukraine, tare da yin tir da kai wa yankunan fararen hula hare hare.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.