Isa ga babban shafi

Yawan makaman nukiliya ya karu a shekarar 2022 - Rahoto

Wani sabon rahoto ya ce yawan makaman nukiliya sun karu a shekarar 2022, lamarin da aka yi ittifakin ya wanzu ne da sa hannun China da Rasha, inda ya kara da cewa tun da aka fara yaki a Ukraine, barazanar nukiliya ta ta’azzara.

Rahoton ya  dora alhakin karuwar makaman nukiliya a kan manyan kasashe da ke da ruwa da tsaki a yakin Rasha da Ukraine.
Rahoton ya dora alhakin karuwar makaman nukiliya a kan manyan kasashe da ke da ruwa da tsaki a yakin Rasha da Ukraine. AP
Talla

Rahoton da wata kungiya mai zaman kanta, ta kasar Norway, wato Norwegian People’s Aid ta wallafa ya ce akwai makaman nukiliyar da za  a iya amfanin da su, wadanda suka kai dubu 9 da 576 a shekarar 2023, abin da ke nufin sun karu daga dubu 9 da 440 da ake da su a shekarar 2022.

Rahoton ya ce wadannan makamai suna da karfin yin  barna da ta kai sama da ta bama-bamai dubu 135 da aka jefa a Hiroshima a lokacin yakin  duniya na 2.

An wallafa wadannan alkalumman ne a daidai lokacin da Rasha ke ci gaba da nanataa barazanar amfani da makaman nukiliya, idan har kasahen yammacin Turaai suka ci gaba da bai wa Ukraine gudummawar makamai don ta kare kanta daga mamayar da ake mata.

A ranar Asabar, shugaban Rasha Vladimir Putin ya sanar da cewa ya cimma yarjejeniya da Belarus don jibge kawarya-kwaryar makaman nukiliya a yankinta.

An dangata Karin makaman nukiliya 139 a duniya a shekarar da ta  gabata  da kasashen Rasha, wadda ta fi yawan  makaman a duniya, inda ya kai  har dubu 5 da 889 sai kuma China, India, Koriya ta Arewa da Pakistan.

Kasashen da ke da karfin nukiliya a hukumance a duniya kuwa sune, Amurka, Rasha, Birtaniya, Faransa, China, India, Paksitan, a yayin da Isra’ila tana da su amma  ba a hukumance ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.