Isa ga babban shafi

Biden ya bukaci Rasha ta saki dan jaridar Amurka

Shugaba Joe Biden na Amurka ya bukaci Rasha ta saki dan jaridar Wall Street Journal da ta kame a jiya alhamis bisa zarginsa da aikata liken asiri, kuma ake tsare da shi a gidan yarin Moscow. 

Dan jaridar Amurka da Rasha ta kama, Evan Gershkovich
Dan jaridar Amurka da Rasha ta kama, Evan Gershkovich AFP - DIMITAR DILKOFF
Talla

Kiran na shugaba Biden na zuwa ne a daidai lokacin da wata kotu a birnin Moscow ta umarci ci gaba da tsare dan jaridar Amurkan Evan Gershkovich har na tsawon wata guda gabanin fara yi masa shari’a bisa zargin sa da aikata leken asiri a Rashan. 

Tun gabanin kiran na Biden, jaridar Wall Street Journal da Gershkovich ke yi wa aiki ta bukaci lallai Rasha ta gaggauta sakin dan jaridar tare da neman Amurka ta kori jakadan Moscow a Washington da dukkanin ‘yan jaridar kasar saboda abin da mahukunta suka aikata. 

Dan jaridar na Amurka ya musanta a gaban kotu cewa babu kanshin gaskiya a zargin da ake masa na leken asirin, amma hukumomin Rasha sun yi mursisi .

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.