Isa ga babban shafi

Kasashe 140 sun cimma matsaya kan karbar haraji daga kamfanoni na duniya

Kusan kasashe 140 ne suka dauki matakin farko don cimma yarjejeniya kan yadda za a raba kudaden harajin da ake samu daga kamfanoni na kasa da kasa, in ji kungiyar bunkasa tattalin arziki ta duniya ta OECD.

Kofar shiga shalkwatar kungiyar OECD da ke birnin Partis na kasar Faransa.
Kofar shiga shalkwatar kungiyar OECD da ke birnin Partis na kasar Faransa. © Francois Mori / AP
Talla

Wasu kasashe 138, wadanda ke da sama da kashi 90 cikin 100 na abin da ake fitarwa na tattalin arzikin duniya, sun amince da daftarin farko na yarjejeniyoyin bangarori daban-daban kan yadda za a rika biyan harajin wadannan kamfanoni da ke gudanar da ayyukansu a duk fadin duniya, biyo bayan tattaunawar kwanaki biyu da kungiyar ta shirya a Paris.

Kamfanoni da yawa, musamman kamfanonin fasaha, a halin yanzu suna iya sauya hanyoyin rubanya riba cikin sauki ga kasashen da ke da karancin haraji.

A yarjejeniyar da OECD ta jagoranta a shekarar 2021, an cimma matsaya kan mafi karancin haraji na kashi 15 bisa 100 kan kasashen duniya da kuma samar da ka'idoji kan yadda za a rika biyan harajin kasashe daban-daban, ta yadda kasashe ba za su yi asara ba.

Amma OECD ta ce matasayar da aka cimma a wannan makon ya ba da damar samar da ci gaba tare da mai tarihi, gat sarin haraji na duniya.

Kasashen sun kuma yi alkawarin amfani da sabbin tsarin dijital a bangaren haraji kafin Disamba 2024 ko kuma fara aiki da yarjejeniyoyin da aka cimma a babban taron na duniya, muddin aka samu hadin gwiwa mutunta matsayar da aka cimma.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.