Isa ga babban shafi

Adadin wadanda suka mutu ya haura dubu daya a Isra'ila

Isra'ila ta sanar da soma yaki da kungiyar Hamas a hukumance, bayan farmakin da ba a taba ganin irinsa ba da kungiyar Islama ta Falasdinu ta kaddamar daga Gaza, wanda adadin wadanda suka mutu ya haura dubu daya.

Wasu 'yan sandan Isra'ila tsare da wasu Falasdinawa a masallacin Al-Aqsa dake birnin Kudus.
Wasu 'yan sandan Isra'ila tsare da wasu Falasdinawa a masallacin Al-Aqsa dake birnin Kudus. © Middle East Eye
Talla

 

 A ci gaba da neman sake kwace iko bayan wannan kazamin hari daga 'Yan kungiyar Hamas,sojojin Isra'ila sun ci gaba da zakulo 'yan kungiyar Hamas a kudancin Isra'ila tare da ci gaba da kai hare-hare ta sama kan wasu wurare a Gaza.

Firaminista Benjamin Netanyahu ya yi kashedi yan lokuta biyo bayan wannan hari wanda ya yi sanadin mutuwar kusan dubu daya a cikin kasa da sa'o'i 48.

Yankin Gaza karkashin ikon yan kungiyar Hamas
Yankin Gaza karkashin ikon yan kungiyar Hamas AP - Ariel Schalit

 

Fiye da mutane 600 aka kashe a Isra'ila tare da raunata 2,000, ciki har da 200 "a cikin mawuyacin hali", a wata sanarwa daga gwamnatin Isra’ila.

 Kakakin rundunar sojojin Isra'ila da yammacin yau Lahadi ya na mai cewa suna tabbacin cewa mayakan Hamas na nan cikin tareda jama’a, jami’in ya kuma da yin alkawarin farautar "'yan ta'adda a duk inda za su kasance".

 

Harin makami mai linzami daga yankin Gaza
Harin makami mai linzami daga yankin Gaza REUTERS - IBRAHEEM ABU MUSTAFA

 

 

  Sojojin Isra'ila sun aike da Karin dakaru da nufin sake samun cikakken ikon yankunan da yan kungiyar Hamas ke iko a kai a zirin Gaza, tare da kubutar da Isra'ilawa da aka yi garkuwa da su.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.