Isa ga babban shafi

Kasashen duniya sun gaza shawo kan matsalar sauyin yanayi

Majalisar Dinkin Duniya ta ce kasashe na gazawa wajen daukar matakan shawo kan matsalar sauyin yanayi,  sakamakon yadda nazarin da ta yi a game da alkawuran da suka dauka na rage hayaki mai gurbata muhalli na nuni da cewa ci gaban da aka samu dan kalilan ne. 

Har yanzu an gaza magance matsalar fitar da hayaki mai gurbata muhalli.
Har yanzu an gaza magance matsalar fitar da hayaki mai gurbata muhalli. REUTERS/Toru Hanai
Talla

 

A wani rahoton da ta fitar ‘yan makwanni gabanin gagarumin taron da ke tafe a kan yanayi,  hukumar kula da abin da ya shafi yanayi ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce duniya ta gaza wajen daukar matakan gaggawa don ganin bayan hayaki mai gurbata muhalli. 

Ganin yadda yanayi ke kara zafi, kuma ake sa ran shekarar 2023 ta kasance mafi zafi a tarihin duniya, masana kimiyya sun ce dole ne a kara matsa wa shugabannin manya kasashen duniya don kawar da hayaki mai gurbata  yaanayi. 

Majalisar Dinkin Duniya ta gano cewa shirin da kasashe  kusan 200  suka yi a game da saukaka dumamar  yanayi zai rage hayaki mai gurbata yanayi a shekarar 2030  da kaso 2 ne kawai idan aka kwatanta da hekar 2019. 

Shugaban kwamitin da ke nazari a batutuwan da suka shafi dumamar yana yi na Majalisar Dinkin Duniya, Simon Stiell ya ce duniya ta kauce hanya a game  da rage dumamar yanayi, saboda haka taron yanayi na COP  28 da za a yi a birnin Dubai na Hadaddiyar Daular Larabawa ne dama ta kawo sauyi a wannan lokaci. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.