Majalisun Dokokin Nigeria sun amince da Namadi Sambo a matsayin mataimakin shugaban kasa
Majalisun dokokin kasar biyu sun amince da nadin da shugaba Dr Goodluck Jonathan ya yi wa Gwamnan Jihar Kaduna Namadi Sambo, a matsyain sabon mataimakain shugaban kasa.Majalisar dattawa ta fara haka daga bisani maramar majalisar wakilai ta bi sahu. Kuma duka sun amince da zabin da gagarumin rinjaye.Kafin wannan sabon mukamun Sambo shi ne gwamnan Jihar Kaduna, tun cikin shekara ta 2007.An samu gibin bayan rasuwar shugaba Umaru Musa YarAdua akan madafun iko, abun da ya janyo rantsar da mataimakainsa Goodluck Jonatahan a matsayin shugaban kasa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: