Isa ga babban shafi
Cote d’ivoire

Gbgbo Ya Hana Gwamnan Banki Sauka

Shugaban kasar Cote D'Ivoire  Laurent Gbagbo yayi fatali da umarnin kasashen Yammacin Afrika na  jiya, dake cewa Gwamnan Babban Bankin Kasar ya sauka daga aiki.Wata sanarwa daga Laurent Gbagbo da aka watsa  ta  gidan  Talabijin  na kasar na cewa kada bangaren Alassane Ouattara ya kuskura ya nada sabon Gwamnan Babban Bankin Kasar kamar yadda Shugabannin Kasashen Yammacin Afrika suka ce yayi.Saboda haka Laurent Gbagbo yace Gwamnan Babban Bankin Kasar Phillip Henry Dakori-Table, kada ma ya tanka ya cigaba da aikin sa.Shugabannin Kasashen yammacin  Afrika na bukatar Gwamnan Babban Bankin daya daya sauka ne saboda yadda ya bari Laurent Gbagbo keta barnata dukiyar kasar.    

Shugaba Laurent Gbagbo
Shugaba Laurent Gbagbo rfi
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.