Isa ga babban shafi
DRC Congo

Thomas Lubanga ya daukaka kara kan hukuncin kotun duniya

Mutumin farko da kotun hukunta manyan laifufuka ta ICC ta samu da laifufukan yaki, a Janhuriyar Demokradiyar Congo, Thomas Lubanga, ya daukaka kara kan hukuncin daurin shekaru 14 da aka masa.  

Thomas Lubanga
Thomas Lubanga REUTERS/Jerry Lampen
Talla

An dai samu tsohon shugaban 'Yan Tawayen ne da hannu wajen sanya kananan yara yaki wanda ya kaiga kashe mutane 60,000 a shekarar 1999.

Tun dai shekarar 2006 da ake tsare da Lubanga a birnin Haque.

A watan Yulin da ya gabata ne aka yankewa Lubanga, dan shekaru 51, hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekaru 14, domin rawar daya taka wajen aikata laifukan yaki.

Rahotanni na nuna cewa akalla mutane sama 60,000 suka mutu a rikicin kasar tun daga shekarar 1999.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.