Manyan kasashen Larabarawa sun amince shiga gasan kwallon kafa a yankin
Akwai alamun kwallon kafa tsakanin kasashen Larabawa zai dinke dukkan sabani da tsamin dangantaka da ake samu yanzu haka tsakanin kasashen Larabawan.
Wallafawa ranar:
Wadannan kasashe ana ganin basa ko ga maciji tsakanin wasunsu.
A yanzu haka kasar Saudiya, da Daular Larabawa da Bahrain za su shiga gasan wasannin kwallon kafa da aka shirya yi a kasar Qatar.
Wadannan kasashen Larabawa uku da kuma kasar Masar sun yanke dankon zumunci da juna a watan shida na shekara ta 2017 saboda kowanne na zargin dan uwansa da marawa ta'addanci da zargin muamulla da Iran da mugun nufi.
Yanzu haka dai kasashen sun nuna lallai dasu za’a yi gasan kwallon kafan kasashen Larabawan.
Za'a fara gasan ne a ranar 24 ga wannan wata da muke ciki zuwa ranar 6 ga watan Disamba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu