Twitter dandali ne na abokantaka da sada zumunci da ake amfani da shi ta intanet wanda ke sada mutum da mutane daga sassan kasashen duniya, kuma ana amfani da dandalin Twitter domin karba da tura sakwanni tare da wanzar da muhawara. Dandalin Twitter wasu Amurkawa ne guda uku suka samar da shi a San Fransisco kasar Amurka wato Jack Dosey da Evans Williams da kuma Biz Stone. Kuma an kaddamar da Twitter a shekarar 2006, tun lokacin ne kuma shafin Twitter ya samu karbuwa a kasashen Turai. An kiyasta cewa sama da mutane miliyan 200 ne ke amfani da dandalin na Twitter a duniya, sai dai kuma a kasashen Africa ba kasafai ake amfani da Twitter ba kamar Shafin dandalin Facebook. Shirin Ilimi Hasken Rayuwa ya yi nazari dangane da yadda ake amfani da Shafin dandalin Twitter tare da bayani akan muhimmancinsa.
Sauran kashi-kashi
-
Taro kan gudummawar kafafen yada labarai a bangaren tsaro a jami'ar ABU Zaria
Matsalar tsaro na daya daga cikin matsalolin da ke addabar Najeriya, musamman ma arewacin kasar, hakan ya sanya sashen koyon aikin jarida na jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria da ke jihar Kaduna ya shirya wani taro gagarumin taro na kasa da kasa domin tattaunawa a kan gudumawar da kafafen yada labarai za su iya bayarwa wajen warware matsalar tsaro. Ya yi wannan ne da zummar taimaka wa kokarin da al'umma ke yi wajen warware wa kansu matsalar tsaron da ke damun su.05/03/202409:57 -
Yadda amfani da komfuta ya shafi kyaun rubutun dalibai
A wannan makon zamu duba yadda ci gaban kimiyya da Ilimi ke zama wani nau’I na koma baya musamman a tsakanin dalibai a Najeriya.Tun bayan samar ko kuma kirkirar na’urar kwamfuta a 1837, da kuma shigowar ta Najeriya karon farko a 1963 sannu a hankali take bazuwa tsakanin jama’a, yayi da kuma ake samun ci gaba ta fannin amfani da ita.31/01/202409:34 -
Gwamnatin Neja na shirin farfado da tsarin karatun makiyaya
Shirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' na wannan makon zai yi duba ne da tsarin karatun 'yayan makiyaya, wato Nomadic Education. Gwamnatin jihar Neja ce ta yi hobbasa don farfado da shirin karatun 'yayan makiyaya a jihar. Shirin zai bai wa makiyaya damar samun ilimi a duk inda suka yi balaguro don inganta makomarsu. Yanzu haka dai shirye-shirye sun yyi nisa a game dfdaa wannan shirin a jihar Neja mai fara da matsalar tsaro sakamakon ayyukan 'yan bindiga da ke kashe mutane da satar su don kudin fansa.19/12/202309:56 -
Iyayen dalibai a Nijar na kokawa kan tsadar kudin karatu
Shirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' na wannan makon tare da Shamsiyya Haruna ya maida hankali ne kan yadda iyaye ke kokawa a jamhuriyar Nijar kan tsadar kudin karatun 'ya'yansu, masamman makaruntu masu zaman kansu saboda matsaloli na tsadar rayuwa da aka shiga tun bayan da sojoji suka yi juyin mulki.14/11/202310:08 -
Najeriya: Yadda tsadar man fetur ke ci gaba da yin tasiri kan harkar ilimi
Shirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' na wannan mako tare da Shamsiyya Haruna ya maida hankali ne kan yadda matsalar tsadar man fetur ke ci gaba da yin tasiri akan harkar ilimi a Najeriya, wanda tun bayan sanar da janye tallafin mai a kasar kanana da manyan makarantu ke daukan matakai daban daban da zummar daidaita harkokinsu a cikin wannan yanayi.31/10/202310:06