Nigeria
An kwana ana jin amon bindigogi a birnin jos, Nigeria
Bayanan kuma dake fitowa daga birnin jos a tarayyar Nigeria na nuna cewa an kwana ana jin karar harbe harbe, da ya sa mazauna birnin suka kwana cikin firgicin. Wasu bayanan sun nuna cewa wasu ne suka yi yunkurin bin dare don kai hari kan wasu anguwannin birnin, inda jami’an tsaro kuma suka yi ta tarwatsa su.A ranar litinin da ta gabata ne wasu mutane suka yi wa masu sallar idi kawanya, suka kuma kai musu hari lamarin da ya yi sanadiyyar rasa rayuka da dama.
Wallafawa ranar: