Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Dan Masanin Kano, Dakta Yusuf Maitama Sule

Wallafawa ranar:

A makon gobe ne Najeriya za ta yi bukin cika shekaru 13 da dawowa mulkin Demokradiya, Kuma yanzu haka ana ci gaba da nazarin ci gaban da aka samu, da kuma matsalolin da ake fuskanta. A lokacin da ya ke gabatar da wata kasida game da tsarin Gwamnatin da ya dace da kasashen Afrika, Tsohon Jakadan Najeriya a Majalisar Dinkin Duniya, Dakta Yusuf Maitama Sule, Dan Masanin Kano, ya bukaci gwamnati mai ci sauka daga karagar mulki watanni shida kafin zabe, don bai wa wadanda ba ‘Yan siyasa ba, damar gudanar da zabe, domin kaucewa magudi.

Dan Masanin Kano, Dr. Yusuf Maitama Sule a Lokacin da yake Hira da Rediyon Faransa
Dan Masanin Kano, Dr. Yusuf Maitama Sule a Lokacin da yake Hira da Rediyon Faransa RFIHausa/bashir
Talla

Barista Solomon Dalung yace Dan Masani ya ba da misalin makiyayi a matsayin shugaba na gari wanda zai hanawa cikin shi ya ba dabbobin da ya ke kiyo.

A cewar Dan Masani sai shugaba ya zama kamar Bafulatani da Dabbobinsa. kuma a cewar shi, kama-karya da Jan Ido da Barazana ba zasu kawo zaman lafiya ba kuma ba za su warware rikici ba sai idan shugaba ya yi kokarin mallakar zukatan mutane kamar yadda Bafulatani ke yin adalci ga dabbobin shi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.