Wasu hareharen kunar bakin wake, sun hallaka mutane dadama a birnin Abuja
A jiya Juma’a wasu jerin fashe-fashen bama bamai guda 2, sun girgiza birnin tarayyar Nigeria Abuja, inda a baya kungiyar Boko Haram ta sha kai wasu jerin hareharen ta addanci.
Wallafawa ranar:
Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasar Nema, ta bayyana hare haren na Jiya da yin sanadiyar mutuwar mutane da dama
Abaya dai wasu hare haren da kungiyar Boko Haram ta dauki alhakin kaiwa a Nyanya dake birnin na Abuja, a shekarar da ta gabata ta 2014 sun sanadiyar mutuwar mutane sama da 90 a yayinda wasu daruruwa suka jikkata
Duk da cewa kawo yanzu babu wanda ya fito ya dauki alhakin kai wannan hari amma ana zargin kungiyar Boko Harm dake ci gaba da tada hankulla akasarda ma makwabtanta da kai harin
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu