Isa ga babban shafi
Najeriya

Sojin Najeriya sun lalata sansanonin Boko Haram

Rundunar sojin Najeriya ta lalata sansanonin biyar da mayakan Boko Haram ke amfani da su a jihar Borno da ke yankin arewa maso gabashin Najeriya.

Sojojin Najeriya da ke yaki da Boko Haram.
Sojojin Najeriya da ke yaki da Boko Haram. AFP PHOTO/HO/NIGERIAN ARMY
Talla

Wata sanarwa da kakakin rundunar sojin Najeriya ya fitar, Kanal Sani Usman ta bayyana cewa, sojoji sun lalalata sansanonin mayakan da ke Hausari da Baranga a karamar hukumar Marte.

Sanarwar ta ce, sojin sun kaddamar da wannan farmakin ne a wani mataki na ci gaba da kokarin kwato wuraren da Boko Haram ta karbe tare da kawo karshen kungiyar.

Sojin Najeriya sun yi nasarar hallaka mayakan Boko Haram biyu a fafatawar da suka yi da juna a sansanonin, baya ga makaman da suka karbe na mayakan kamar yadda sanarwa ta bayyana.

Har ila yau sanarwar ta ce, a watan jiya ne runduna ta 5 ta lalata sansanonin Boko Haram guda 20 a yankin Kerenowa.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.