Isa ga babban shafi
Najeriya

Kotun kolin Najeriya ta dakatar da shari'ar Saraki

Kotun koli ta Najeriya ta dakatar da shari’ar da kotun kula da da’ar ma’aikata ke yi wa shugaban majalisar dattawan kasar, Bukaola Saraki.

Shugaban majalisar dattawan Najeriya, Sanata Bukola Saraki.
Shugaban majalisar dattawan Najeriya, Sanata Bukola Saraki. ynaija.com
Talla

Gabanin wannan matakin dai, manyan kotunan kasar sun yi watsi da karar da Saraki ya shigar musu na neman dakatar da shari’ar da ake yi masa.

Kotun kolin ta ce, a dakatar da shari’ar har nanda wani lokaci kafin ta yanke hukuncin karshe game da karar da ya shigar mata.

Ana tuhumar saraki da aikata laifuka 13 da ya hada da bayar da bayanan karya kan kadarorin da ya mallaka, duk da dai ya musanta zargin.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.