Saraki ba zai yi murabus ba- Ndume
Jagoran majalisar dattawan Najeriya, Ali Ndume ya bayyana cewa, shugaban majalisar Bukola Saraki ba zai yi murabus ba daga mukaminsa har sai kotun ladabtar da ma’aikata ta kasar ta same shi da aikata laifin da ake zarginsa akai.
Wallafawa ranar:
Ndume ya shaida wa manema labarai haka ne a fadar shugaban kasar da ke birnin Abuja bayan ya kammala ganawa da mukaddashin shugaban kasar, Yemi Osinbajo a jiya Talata.
Har ila yau, Ndume wanda ya samu rakiyar Dino Melaye da Abdullahi Adamu ya bayyana kiraye-kirayen da ake yi na cewa Saraki ya sauka daga kujerarsa a matsayin garaje, sannan ya ce, kuskure ne a caccake sa kafin kotun ta same shi da laifi
Saraki dai na fuskantar tuhuma ne sakamakon zargin da ake yi masa kan bayar da bayanan karya dangane da kadarorin da ya mallaka a lokacin da ya ke gwamnan jihar Kwara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu